![An Nada Lampard A Matsayin Sabon Kocin Coventry City](https://iqra-media.s3.eu-west-2.amazonaws.com/public/57C77D81-B3FE-4F0C-92CB-99BE2682F2A2_w1023_r1_s__ScaleWidthWzEwMDBd.jpg)
Lampard ya maye gurbin Mark Robins, wanda aka sallama a farkon wannan watan.
washington dc —An nada tsohon dan wasan tsakiya na kungiyar kwallon kafar Chelsea da kasar Ingila Frank Lampard ya zamo kociyan Coventry a bisa yarjejeniyar shekaru 2 da rabi, a cewar kungiyar.
Lampard ya maye gurbin Mark Robins, wanda aka sallama a farkon wannan watan.
Coventry na mataki na 17 a gasar zakarun bayan wasanni 17 inda suka yi rashin nasara a wasanninsu 4 na karshe.
A matsayinsa na dan wasa, Lampard ya ciwa Chelsea kwallaye 211 a dukkanin gasar da ta buga a shekaru 13 da ya shafe a cikinta masu cike da daukar kofi.
Ya taba horas da kungiyoyin Chelsea da Everton a gasar firimiya, haka kuma ya horas da kungiyar Derby County.
Lampard zai karbi ragamar horas da Coventry a karon farko ran Asabar mai zuwa inda za ta kara da kungiyar Cardiff City a filin wasa na Coventry Building Society.