Sojojin Somaliya sun halaka mayakan Al-Shabab 70

Ma'aikatan yada labaran da ke a birnin Modagishu ta sanar da cewa sojojin gwamnatin sun kwace motocin yaki masu sulke da makamai da dama daga mayakan na Al-Shabab a jihar Hirshabelle da ke kudancin Somaliya.

Karin bayani:An kashe 'yan al-Shabab a Somaliya 

Shaidun gani da ido a yankin sun tabbatar da ganin gawarwakin mutanen da aka kashe akalla 70, duk da cewa kamfanin dillancin labarai na AFP bai gama tantance bayanan da hukumomi da shaidun gani da ido suka bayar ba.

Karin bayani: Sojin Amirka sun kai wa al-Shabaab hari

Tun a shekara ta 2011, dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar Tarayyar Afirka AU suka fatattaki mayakan Al-Shabab daga birnin Mogadishu, inda kuma suka kafa sansanoni a yankunan karkara.

 


News Source:   DW (dw.com)