Shugaban Kwango zai tattauna kafa gwamnatin hadin kan kasa

A cewar kwararru na Majalisar Dinkin Duniya, kungiyar yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan sojoji 4,000 daga makwabciya kasar Rwanda, tun a watan Janairu suke jagorantar bore a kasar ta tsakiyar Afirka.

Yan tawayen sun kama birnin Goma da ke gabashin kasar mai mutane kimanin miliyan biyu yayin da kuma aka kashe mutane kusan 3,000

Bugu da kari yan tawayen sun kuma kama garin Bukavu da ke da mutane fiye da miliyan daya .

Fada tsakanin sojojin Kwango da yan tawayen M23 na haifar da fargaba ta fadada yaki a fadin yankin.

 


News Source:   DW (dw.com)