Robert Habeck ya yanke kauna da jagorantar Greens

A cikin tattausar lafazi Mr. Habeck ya shaidawa manema labarai cewa jam'iyyar The Green ta fadi kasa warwas da kashi 11.6 bisa 100 sabanin tagomashin da jam'iyyar ta samu a zaben 2021, inda ta samu kashi 14.7 bisa 100. Ya kuma kara da cewa wannan ba sakamako bane mai kyau da jam'iyyar za ta yi tinkaho da shi.

Karin bayani: Jam'iyyar the Greens, na son sake sabon lale 

Rashin nasarar jam'iyyar Greens na nufin cewa Robert Habeck zai rasa mukaminsa a gwamnati, kasancewar Friedrich Merz na kawancen jam'iyyar CDU/CSU shi ne zai kafa gwamnati tare da kawancen jam'iyyar SPD ta Shugaban Gwamnatin Jamus mai barin gado Olaf Scholz.

Karin bayani:  Jamus: The Greens ta amince da shirin kafa gwamnati

Mr. Habeck da sauran jagororin jam'iyyar The Greens sun yi amannar cewa duk da rashin nasarar da jam'iyyarsu ta fuskanta a zaben, ta dara jam'iyya mai mulki ta SPD wacce ta samu mummunar koma baya a tarihinta.

 


News Source:   DW (dw.com)