Ministan harkokin kasashen waje na Yugandan Henry Oryem ne ya sanar da hakan ga kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP, inda ya ce sun tura sojojinsu zuwa Bunia da ke zaman babban birnin gundumar Ituri a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwangon wanda Yugandan ta jima da jibge sojojinta karkashin wata yarjejeniya da Kinshasa. Matakin sojojin Yugandan na zuwa ne bayan 'yan tawayen na M23 da Ruwanda ke goyon baya sun kwace wani gari da ke makwabtaka da gundumar Kivu ta Kudu daga arewaci, abin da ke kara fargabar barkewar yaki a tsakanin kasashen yankin baki daya.
News Source: DW (dw.com)