Shugaban hukumar kare hakkin bil Adama ta Majalisar Dinkin Duniya, Volker Turk ya ce jami'an Bangladesh sun aikata laifukan take hakkin dan Adam ne a lokacin da suke kokarin murkushe zanga-zangar da ta hambarar da gwamnatin Sheikh Hasina a bara.
Karin bayani: An kashe masu zanga-zanga a Bangladesh
Da yake gabatar da sakamakon binciken da aka gudanar, wanda ya hada da shaida daga manyan jami'an Bangladesh, rahoton ya nuna manufar hukumomin na kai hari, da murkushe masu zanga-zangar adawa da gwamnati. Rahoton ya kuma yi nuni da cewa a kalla mutane 1,400 ne aka kashe yayin tarzomar, wadda ta samo asali bayan da dalibai suka yi bore kan yadda ake kason ayyaukan a ma'aikatun gwamnati, inda daga bisani ta rikide zuwa ta gama-gari. Sheikh Hasina dai ta hau kan karagar mulkin kasar ne daga shekarar 1996 zuwa 2001 inda ta sake mulkar kasar daga 2009 zuwa 2024.