Kamfanin dillancin labarai na AFP ya shaida wasikar bukatar dauki da jakadan Kwango a Majalisar Dinkin Duniya Zenon Mukongo ya gabatarwa zauren kwamitin sulhu na majalisar, biyo bayan hare-haren da 'yan tawayen M23 suka kaddamar a lardin Kivu da ke gabashin kasar.
Karin bayani: MDD ta yi gargadi kan rikicin Kwango
Jakadan ya ce gwamnatinsu ta samu rauni sakamakon rashin bada kulawar gaggawa daga majalisar, tun lokacin da 'yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Ruwanda suka kwace iko da babban birnin Goma na Arewacin Kivu da kuma Bukavu na lardin Kudancin Kivu.