Kwalambiya ta nemi 'yan kasar marasa takardu komawa gida daga Amurka

Shugaba Gustavo Petro na kasar Kwalambiya a wannan Jumma'a ya bukaci 'yan kasarsa da ke zaune a kasar Amurka ba tare da takardun izini ba, kan su dawo gida Kwalambiya na take.

Karin Bayani: Mayakan FARC sun kashe sojojin Kwalambiya

A cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta shugaban ya ce akwai wani shirin da gwamnatin Kwalambiya ta kirkiro na ba da racen kudi ga 'yan kasar da suka dawo daga Amurka bisa wani shiri na ganin sun samu wata damar bunkasa rayuwarsu idan suka dawo gida.

Ita dai kasar Kwalambiya da ke ynakin Latin Amurka tana cikin wadanda suka fara fito na fito da Shugaba Donald Trump na Amurka kan mayar da 'yan kasar Kwalambiya zuwa gida wadanda suke zaune a Amurka a tare da takardun zama ba.

 


News Source:   DW (dw.com)