Kasashen Turai na rige-rigen zuwa Siriya

Ziyarar ta ministan harkokin kasashen ketare na Italiya Antonio Tajani na zaman ta baya-bayan nan wacce jami'an diplomasiyyar kasashen Turai ke kai wa Siriya, tun bayan kifar da gwamnatin kama-karya ta Bashar al-Assad a watan Disambar bara. Koda yake kamfanin dillancin labaran Siriyan SANA bai yi wani karin haske kan abin da Tajani da Ahmed al-Sharaa suka tattauna ba wata guda bayan jagoran kungiyar masu ikirarin jihadin ya kwace iko da fadar gwamnati ta Damascus, abin da  ya tilasta Assad tserewa zuwa Moscow.

 

 


News Source:   DW (dw.com)