Kamfanin dillancin labaran kasar ta Hadaddiyar Daular Larabawa WAM ne ya ruwaito hakan, inda ya ce kalaman na Shugaba Sheikh Mohammed bin Zayed na zuwa ne sakamakon kudurin shugaban Amurka Donald Trump na kwace iko da yankin Zirin Gaza na Falasdinu tare da raba mazauna yankin zuwa kasashe makwabta.
Gaza: Cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
To view this video please enable JavaScript, and consider upgrading to a web browser that supports HTML5 video
02:06Al Nahyan ya bayyanawa sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio da ke ziyara a yanzu haka a birnin Abu Dhabi bayan kai ziyara a Isra'ila da Saudiyya cewa, yana da muhimmanci a alakanta gyaran yankin na Zirin Gaza da matakin kawo karshen rikicin Isra'ila da Falasdinu na din-din-din ta hanyar samar da kasashe biyu.
Falasdinawa a Gaza na cikin mawuyacin hali
Adadin wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata a Gaza na karuwa yayin da Isra'ila ke ci gaba da daukar fansa na hare-haren ta'addancin Hamas.
Hoto: Fatima Shbair/AP/picture allianceIsra'ila ta tsananta hare-haren ramuwar gayya a Gaza
Isra'ila ta tsananta kai hare-hare ta sama a zirin Gaza kwanaki bayan da Hamas ta kaddamar da hare-hare. Kungiyar EU da Amurka da sauran kasashe sun ayyana Hamas mai iko da Gaza a matsayin kungiyar ta'addanci. Firayiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce "abin da za mu yi wa makiyanmu a cikin kwanaki masu zuwa za a jima ba a manta ba."
Hoto: Belal Al SabbaghAFP/Getty ImagesAn lalata gine-gine masu yawa
Daruruwan gine-gine ne suka lalace gaba daya, daura da wasu dubbai da suka lalace sosai sakamakon hare-haren Isra'ila, a cewar ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya (OCHA). Dubban mutane ne aka ce ba su da ruwa.
Hoto: Mohammed Talatene/dpa/picture allianceNeman wadanda suka makale
Masu aikin ceto na neman wadanda suka tsira bayan harin da Isra'ila ta kai kan sansanin 'yan gudun hijira na Jabalia da ke arewacin Gaza. Ya zuwa yanzu, sama da mutane 1,000 suka mutu yayin da wasu fiye da 5,000 suka jikkata bayan hare-haren jiragen sama a yankin da ke karkashin ikon Hamas, a cewar hukumomin yankin.
Hoto: Mahmud Hams/AFP/Getty ImagesMakokin wadanda suka mutu
Wata mata ta yi kuka yayin da aka dora gawarwaki a kan babbar mota, bayan wani harin da Isra'ila ta kai. A cewar hukumar lafiya ta Gaza, an kashe fiye da yara 200 da mata sama da 100 a Gaza.
Hoto: Said Khatib/AFP/Getty ImagesAn rufe Gaza
Falasdinawa na tserewa harin Isra'ila. A cewar Majalisar Dinkin Duniya, fiye da mutane 187,000 ne a Gaza suka rasa matsugunansu, kana sama da dubu 100 suka yi mafaka a makarantun MDD, yayin da wasu 40,000 suka kaurace wa gidajensu. Shi kansa ficewa daga zirin Gaza abu ne mai wuya kasancewar Isra'ila ta rufe yankin tare da rufe mashigar Masar.
Hoto: Saleh Salem/REUTERSSojojin Isra'ila suna iko da iyakar Gaza
Ana ganin sojojin Isra'ila suna sintiri a kan iyakar Isra'ila da Gaza. Mayakan Hamas sun kutsa shingen kan iyaka a wurare da dama a cikin daren ranar 7 ga watan Oktoba kafin su kai hare-hare a yankin Isra'ila. Isra'ila ta gina shinge kan iyakar Gaza a shekara ta 1994. An kuma rufe kan iyakar Gaza da Masar da dogon shinge.
Hoto: Oren Ziv/AP/picture allianceSojojin Isra'ila su na kan iyakar Gaza
Bayan da Isra'ila ta fitar da karin sojoji 300,000, mazauna Gaza da dama na fargabar cewa, akwai yiwuwar kaddamar da harin Isra'ila ta kasa. Motocin soji da kayan yaki sun cika kan iyakar Gaza. An kwashe kusan dukkan mautanen da ke garuruwan Isra'ila da ke kan iyaka da Gaza gaba daya.
Hoto: Ilia Yefimovich/dpa/picture allianceMummunan yanayi na bukatar jinkai
Da yake magana da CNN, Jan Egeland, babban sakataren hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Norway, ya yi gargadin tagaiyarar al'umma a Gaza. "Zai kai ga aikata laifukan yaki idan yara za su mutu da yunwa a asibitoci saboda rashin wutar lantarki misali,"
Hoto: Mahmud Hams/AFP/Getty ImagesShugaban Hamas a Gaza, Yahya Sinwar
Yahya Sinwar ya kasance shugaban kungiyar Hamas a Gaza tun a shekarar 2017. Ana masa kallon daya daga cikin wadanda suka shirya harin ta'addancin da aka kai kan Isra'ila a ranar 7 ga watan Oktoba. An ambato Sinwar, wanda ya taso a sansanin 'yan gudun hijira na Gaza yana cewa, "gwamma mu mutu a matsayin shahidai da mu mutu saboda zalunci da wulakanci."
Hoto: Mohammed Abed/AFPTsanantar tashe-tashen hankula
Wani mai magana da yawun Hamas ya shaida wa manema labarai cewa, a duk lokacin da Isra'ila ta kai hari a kan fararen hula a Gaza ba tare da yin gargadi ba, to za a kashe daya daga cikin 'yan Isra'ila da ake garkuwa da su. Ministan harkokin wajen Isra'ila Eli Cohen ya yi gargadin cewa babu yafiya kan irin wannan mataki.
Hoto: Mahmud Hams/AFP/Getty ImagesMatakin na Hadaddiyar Daular Larabawa kan wannan rikici na da matukar muhimmanci, kasancewarta guda cikin Kasashen Larabawa hudu da suka kulla kawance da Isra'ila a lokacin mulkin Trump na farko da kuma yadda ta taka rawa wajen sake gina Gazan a lokutan baya.