Iran ta tsare wasu 'yan kasar Burtaniya guda biyu bayan zarginsu da aikata laifukan da suka shafi tsaro, kamar yadda ma'aikatar harkokin wajen Burtaniya ta sanar ranar Alhamis.
Karin bayani:Iran ta yi allawadai da hare-haren da Amurka da Burtaniya suka kai Yemen
Kafar yada labaran Iran IRNA ta rawaito cewa jakadan Burtaniya a Iran Hugo Shorter ya samu zarafin tozali da mutane biyun da aka kama a lardin Kerman, kuma yana ci gaba da tuntubar hukumomin Tehran a kan batun, to sai dai babu wani karin bayani a kan ganawar.
Karin bayani:Kasashen G7 na shirin kakabawa Iran takunkumi saboda Isra'ila
Iran dai ta yi kaurin suna wajen kama 'yan kasashen waje da tsare su a matsayin fursunonin siyasa, wadanda har yanzu babu alkaluman adadin mutanen da ta cafke, to amma ta yi togaciyar cewa tana kama su ne bisa aikata laifin leken asiri.