Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken wanda ya kai ziyara Jordan ya baiyana muhimmancin kauce wa duk wani abu da zai sake tada rikici a Syria.
Ya yi kalaman ne bayan sanar da cewa a baya bayan nan Israila da Turkiyya sun kai hari cikin Syria. Ya ce Amurka na son tabbatar da cewa ba a yi amfani da Syri a matsayin sansanin yan ta'adda da kuma tada hankalin kasashe makwabtanta ba.
A waje guda kuma Shugabannin kungiyar kasashen G7 masu karfin tattalin arziki na duniya sun ce a shirye suke su taimaka wa shirin da zai samar da gwamnati mai nagarta wadda za ta kunshi kowa da kowa a Syria ba tare da nuna bangaranci ko addini a sha'anin gudanarwar gwamnati ba.