A mako mai zuwa ne firaministan Burtaniya Keir Starmer zai gana da shugaban Amurka Donald Trump a ziyarar da Mr Starmer zai kai birnin Washington, DC, kamar yadda ofishin firaministan a London ya tabbatar.
Karin bayani:An kori jami'in diflomasiyyan Birtaniya daga Rasha
Gwamnatin Burtaniya na kokarin samun daidaiton ra'ayi da sabuwar gwamnatin Amurka ta Trump, wadda ke da ra'ayin janye agazawa kawancen kungiyar tsaro ta NATO da irin matakin da yake dauka kan yakin Ukraine da Rasha ba tare da tuntubar kasashen yamma ba.
Karin bayani:Burtaniya ta bukaci Turai ta taka rawar gani a kungiyar tsaro ta NATO
Haka zalika Mr Trump na shirin kara kakaba karin haraji kan kayayyakin Burtaniya da ake shigarwa Amurka, baya ga sabanin da ke neman kunno kai tsakanin kasashen biyu kan tsibirin Chagos da ke karkashin ikon Burtaniya.