Faransa ta hannata wa Chadi sansanin sojinta na karshe a yankin Sahel a jiya Alhamis a yayin wani biki da aka gudanar a asirce wanda ke kawo karshen zaman dakarun Faransar a wannan kasa da ta samu 'yanci kai shekaru 65 da suka gabata.
Hedikwatar tsaron Chadi ta ce mika sansanin da ake wa lakabi da 'Sergent Adij Kossei' da ke birnin N'Djamena ya kawo karshen zaman sojojin Faransa a kasar tun bayan zuwansu a karon farko a shekarar 1.900 a lokacin fara mulkin mallaka.
Kakakin hedikwatar tsaron Faransa Kanal Guillome Vernet ya ce an kwashe illahirin ma'aikata da kayan yankin da ke sansanin sojin, kana kuma za a tattare sauran komatsen da suka rage nan zuwa gaba.
Karin bayani: Faransa ta fara kwashe sojinta daga Chadi bayan yanke hulda
A watan Nowamban bara ne dai mahukuntan Chadi suka bukaci ficewar sojojin Faransa su kusan 1,000 daga kasar bayan da shugaba Mahamat Idriss Deby ya bayyana yarjejeniyar tsaro da ke tsakanin kasashen biyu a matsayin 'tsohon yayi'.