Faransa ta sanar da cewa kungiyar tarayyar Turai EU na aikin kokarin janye wa Syria takunkumen da ke kanta, bayan da 'yan tawayen HTS suka hambarar da gwamnatin kama-karya ta Bashar al-Assad a cikin watan Disamban 2024.
Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noel Barrot ne ya bayyana hakan yayin taro a birnin Paris, inda ya ce tun a cikin watan Janairun da ya gabata shi da sauran takwarorinsa na EU suka amince da dage takunkumin karya tattalin arziki da ke kan Syria, domin bata damar tada komadarta, musamman a fannin makamashi.
Karin bayani:Faransa ta ba da sammacin kama Bashar al-Assad
Shi ma ministan harkokin wajen Syria Asaad al-Shaibani ya samu damar halartar taron tattauna batun a karon farko a hukumance a nahiyar Turai, bayan halartar taron tattalin arziki na duniya na birnin Davos a watan Janairun da ya gabata.
Sanarwar da fadar mulkin Faransa ta fitar ta ce nan gaba ne shugaban Emmanuel Macron zai gabatar da jawabi a taron, wanda ke samun wakilcin Amurka da Jamus da Burtaniya, sai tarayyar Turai da Majalisar Dinkin Duniya da kasashen yankin Gulf, har ma da Turkiyya.
Karin bayani:Za a sake bude filin jirgin saman birnin Damascus na Syria
Kasashen yamma na nuna damuwa kan alkiblar da sabon shugaban rikon kwaryar Syria zai jagoranci kasar a kai, musamman ma ta bangaren bai wa tsirarun kabilu da addinai da kuma mata 'yancin walwalwa.