Mayakan 'yan tawayen M23 na kasar Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango sun bayyana shirin kara dausawa zuwa wasu yankin kasar bayan karbe iko da birnin Goma fadar lardin arewacin Kivu daga hannun dakarun gwamnati. Mayakan 'yan tawayen da ke smaun goyon kasar gwamnatin kasar Ruwanda sun ce za su nausa zuwa birnin Kinshasa fadar gwamnatin kasar ta Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango.
Karin Bayani: Rikicin Jamhuriyar Kwango da Ruwanda ya yi kamari
Masu tserewa daga rikicin Jamhuriyar Dimukuradiyyar KwangoHoto: JOSPIN MWISHA/AFPIta dai kasar Ruwanda ta ce burinta shi ne kakkabe mayakan da ke da hannu a kisan kare dangin da ya faruwa a kasar ta Ruwanda a shekarar 1994, amma ana zargin Ruwanda da hannu a rikicin saboda albarkatun karkashin kasa da ake sacewa da hannunta a kasar ta Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango. Rikicin na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ya janyo kungiyar kasashen kudancin Afirka kiran taro a birnin Harare na kasar Zimbabuwe a wannan Jumma'a.