Amurka ta jaddada goyon baya ga al'ummar Koriya ta Kudu

Shugaba Biden ya bayyan kwarin gwiwa na cewar kawancensu zai ci gaba da kasancewa a kan gaba wajen samar da zaman lafiya a yankin Indo-Pacific.

Kazalika Biden ya bayyana jin dadinsa ga dorewar dimukradiyya da bin doka da oda, ya kuma jaddada wa al'ummar Koriya ta Kudu Amurka na tare da su.

A ranar Asabar ce majalisar dokokin kasar ta tsige shugaba Yoon daga madafun iko, bayan yunkurin samar da wata dokar soji da ta bar baya da kura a wani mumunan rikicin siyasa da kasar ba ta ga irin shi ba a baya-bayan nan.

Firaminista Han Duck-soo zai ci gaba da zama mukaddashin shugaban kasa har sai kotun tsarin mulki ta kammala hukuncin ta a kan matakin majalisar.  

Karin Bayani: Rikicin siyasa ya rincabe a Koriya ta Kudu


News Source:   DW (dw.com)