
Shugaban kwamitin, Benjamin Kalu, wanda shi ne mataimakin shugaban Majalisar wakilai, ya bayyana haka a zaman majalisar.
Kalu ya ce buƙatun sun haɗa da 6 daga Arewa ta Tsakiya, 4 daga Arewa ta Gabas, 5 daga Arewa ta Yamma, sai kuma 5 daga Kudu maso Gabas da 4 daga Yankin Kudu maso Kudu da 7 daga Kudu maso Yamma.
Ga jerin buƙatun kamar yadda Kalu ya bayyana.
- Jihar Okun daga Kogi
- Jihar Okura daga Kogi
- Jihar Confluence daga Kogi
- Jihar Benue Ala daga Benue
- Jihar Apa daga Benue
- Jihar FCT daga FCT
- Jihar Amana daga Adamawa
- Jihar Katagum daga Bauchi
- Jihar Savannah daga Borno
- Jihar Muri daga Taraba.
- Jihar New Kaduna daga Kaduna
- Jihar Gujarat daga Kaduna
- Jihar Tiga da Ari daga Kano
- Jihar Kainji daga Kebbi
- Jihar Etiti da Orashi a yankin Kudu maso Gabas
- Jihar Adada daga Enugu
- Jihar Orlu da Aba daga Kudu maso Gabas
- Jihar Ogoja daga Cross River
- Jihar Warri daga Delta
- Jihar Ori da Obolo daga Rivers
- Jihar Torumbe daga Ondo;
- Jihar Ibadan daga Oyo
- Jihar Lagoon daga Lagos
- Jihar Ijebu daga Ogun
- Jihar Oke Ogun/Ijesha daga Oyo/Ogun/Osun
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI