Me Tinubu ya yi da za a sake zaɓen shi - Atiku

Me Tinubu ya yi da za a sake zaɓen shi - Atiku

Aminiya ta ruwaito George Akume na cewa ’yan Arewa ’yan Jam’iyyar APC mai mulki da ke son neman shugabancin kasa su hakura zuwa 2031, saboda a cewarsa, yanzu lokacin mulkin ’yan yankin Kudu ne, don haka su jira sai Tinubu ya kammala wa’adinsa na biyu.

Ya kuma bukaci Atiku, babban abokin hamayyan Tinubu a zaben 2023 daga babbar jam’iyyar adawa ta PDP ya hakura ya jira 2021.

Akume ya ci gaba da cewa idan Allah Ya nufi tsohon mataimakin shugaban kasan da zama shugaban kasa zai zama, ko da yana dan shekara 90 ne.

Amma a martanin Atiku, ya bayyana cewa zabin shugaban kasa abu ne da ke  hannun ’yan Nijeriya zu zabi wanda suke so.

Ya bayyana kalaman Akume a matsayin rashin adalci, domin a halin yanzu, ’yan yankin Kudu sun mulki Nijeriya na tsawon shekara 17 ne — takwas a karkashin Obasanjo, biyar a hannun Jonathan da kuma hudu a hannun Tinubu — idan aka kwatanta da ’yan Arewa da suka yi shekara 11, uku na Yar’Adua da takwas na Buhari.

Atiku ta hannun kakakinsa, Paul Ibe, ya kara da cewa hakan rashin adalci ne, yana mai bayyana cewa zabin shugaban kasa na hannun ’yan kasa yake, sai kuma irin shugabancin da gwamnati mai ci ta yi.

Paul Ibe ya ce, abin tambaya shi ne, “Shin mme Gwamnatin Tinubu ta yi da ’yan Nijeriya za su kara zaben ta?”

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Hulda da mu

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI


News Source:   RFI (rfi.fr)