
A watan da ya gabata ne Kungiyar dalibai da wasu kungiyoyin kare hakokin ma’aikata a kasar suka shirya zanga-zangar nuna adawa da kason aikin ma'aikata wanda ya rikide zuwa kisa bayan wani farmakin da 'yan sanda suka kai, inda aka kashe mutane 206 a cikin kwanaki na tashin hankali kamar yadda alkaluman 'yan sanda da na asibiti na AFP suka nuna.
Mataimakin kwamishina Junaed Alam Sarkar ya tabbatar da sallamar wadanan dalibai da ake tsare da su ga iyalansu. A ranar Juma’ar da ta gabata ne jami’an tsaro na farin kaya suka kama Nahid Islam Shugaban dalibai da wasu mutane biyu a wani asibiti da ke Dhaka babban birnin kasar, inda aka kama su,aka kuma isa da su wani wuri da ba a sani ba. Mahaifinsa Badrul Islam ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa Nahid ya koma gida ne da yammacin yau Alhamis.
An kuma tsare wasu mutane uku inda gwamnati ta ce a lokacin an tsare su ne domin kare lafiyarsu. Ministan shari'a Anisul Huq ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa a yau Alhamis cewa dukkaninsu shida sun ba da kansu don kasancewa a hannun 'yan sanda.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI