Kamar yadda bayanai suka tabbatar, anan ne ake sa ran sakin wasu daga cikin Yahudawan da ke tsare a hannun hamas, bayan mika Agam Berger ga kungiyar agaji ta Red Cross a Jabalia.
A ranar 17 ga watan Oktoban bara ne, harin saman da Isra'ila ta kaddamar a arewacin Gaza ya rutsa da Yahya Sinwar.
Tun da farko dai sai da Isra'ila ta gudanar da bincike domin tantance kwayoyin halittan shugaban na Hamas kafin tabbatar da mutuwarsa.
Kamar yadda bayanai suka a wancan lokacin, sakamakon farko-farko na gwajin kwayoyin halittar ya nuna cewa, Sinwar ɗin ne Isra'ila ta kashe kamar yadda ta tabbatar wa Amurka.
Isra'ila ta ɗauki gawar Sinwar zuwa Birnin Kudus domin gudanar da bincike a kanta bayan harin da ta kai cikin wani gida da shugaban na Hamas da muƙarrabansa ke ciki.
Karo na uku kenan da aka yi musayar fursunoni tsakanin bangarorin biyu, tun daga lokacin da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI