Yayin ganawa da Sarki Abdallah na Jordan wanda ya ziyarce shi a Washington, Trump yace yana da yakinin cewar za su samu fili a ƙasashen Jordan da Masar inda za'a kai Falasɗinawan da za'a kwashe daga Gazar.
Shugaban ya ce bayan kammala tattaunawar da suke yi za'a samu wurin da za'a aje Falasɗinawan dake Gaza da za su zauna cikin farin ciki.
Yayin tsokaci akan matsayin Trump, Sarki Abdallah wanda ya bayyana cewar ƙasarsa za ta kwashi ƙananan yara 2,000 daga Gaza zuwa Jordan, ya kara da cewar Masar za ta gabatar da shirin da suke da shi dangane da makomar Gazar.
Sarkin ya kuma ce akwai wani taron shugabannin kasashen Larabawa da Saudi Arabia za ta jagoranta wanda zai kunshi kasashen su duka domin daukar matsayin bai ɗaya.
Kamfanin dillancin labaran Reuters ya ruwaito cewar kashi 74 na Amurkawa ba sa goyan bayan wanann shiri na Trump wanda zai raba Falasdinawa daga Gaza.
Rahotanni sun ce ƙasashen Jordan da Masar na fargabar rasa tallafin kudaden da suka saba samu daga Amurka domin gudanar da harkokin su na yau da kullum idan suka bijirewa shirin na Trump.
Jordan na samun kudin tallafin da ya kai Dala biliyan 1 da miliyan 450 kowacce shekara daga Amurka, abinda ya sanya ta cikin manyan kawayen ta a yankin Gabas ta Tsakiya.
Daya daga cikin shugabannin Falasdinawa Mustafa Barghouti ya bayyana Trump a matsayin wanda ya gurgnta yarjejeniyar tsagaita wutar da Isra'ila ta kulla da kungiyar Hams da kuma bada damar gudanar da kisan kara dangi akan Falasdinawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI