Shugaban Congo da na Rwanda za su gana a kan rikicn ƴan tawayen M23

Shugaban Congo da na Rwanda za su gana a kan rikicn ƴan tawayen M23

Kagame da Tshisekedi za su halarci taron ƙungiyar ƙasashen yankin gabashin Afrika a birnin Dar es Salam na Tanzania, inda jagoroin yankin su 8 da na kudancin Afrika 16 za su gana.

Ƙungiyar ƴan tawayen M23, wadda Rwanda ke mara wa baya ta karɓe iko da yankuna da dama a yankin gabashin Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo mai ɗimbin arzikin albarkatun ƙasa sakamakon hare-harenta da su ka  ɗaiɗaita dubban mutane.

A makon da ya gabata ne ƙungiyar ta ƙwace birnin Goma mai matuƙar mahimmanci, kuma yanzu haka tana ƙoƙarin rankayawa  lardin ƙudancin Kivu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Hulda da mu

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI


News Source:   RFI (rfi.fr)