A dai dai lokacin da damuna ke faɗuwa a Madagascar masana sun yi gargaɗi kan haɗarin yiwuwar fuskantar zaftarewar ƙasa batun da ya sanya gwamnatin kasar ɗaura ɗamarar wayar da kan jama’a ƙari kan amsawa kuwwa aƙalla 500 da ta sanya a tsaunin Manjakamiadana don ankarar da mazauna wani yanki na birnin Antananarivo da cikin hadari.
Fadar gwamnatin ƙasar ta Madagascar na sahun yankunan da ke fuskantar zaftarewar laka wanda ke haddasa asarar rayuka a kowacce damuna, dalilin da ya sanya mahukuntan ƙasar sanya haramcin yin gini mai ƙarfi ko kuma na dindindin a yankunan da ke gab da tsaunin, face gine-ginen wucin gadi.
Dr Lalah Christian Andriamirado ƙwararriya haɗarin ƙarƙashin ƙasa ta ce zaftarewar laka ka iya rushe aƙalla gidaje 400 sai dai ta shawarci mahukuntan Madagascar kan su samar da wadatattun magudanan ruwa a yankin wanda ta ce za su saukaka ibtila’in.
Hukumar kula da yanayi a Madagascar ta yi hasashen samun doguwar damuna a bana wadda a cikin za a yi ta samun ƙaƙƙarfan ruwan sama akai akai baya ga guguwa mai ƙarfi har sau 5 da za a gani cikin damunar ta bana.
Wannan gargaɗi tuni ya sanya mazauna gefen tsaunin a fargaba, musamman ganin irin ɓarnar da makamanciyar zaftarewar lakar ta haifarwa yankin a shekarar 2019, wanda sai a yanzu ne wasu ke komawa muhallansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI