Mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar, Amina J. Muhammad, wadda ke bayyana wannan takaicin, lokacin da take gabatar da jawabi ga kwamitin sulhu na Majalisar, ta bayyana ta’addanci a matsayin babbar barazana ga zaman lafiya da ya mamaye nahiyar Afirka.
Ta ce wannan kalubale ya haifar da illa mai munin gaske ga shirin samar da ci gaba mai dorewa a nahiyar.
A cewar mataimakiyar magatakardar, yankin Kudu da Hamadar Sahara na dauke da kusan kashi 59 cikin 100 na mace-macen da ke da nasaba da ayyukan ta’addanci a duniya.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce yankin Sahel ne kan gaba wajen fama da yake-yake mafiya muni, tare da kiyasin sama da mutum 6,000 ne suka mutu sakamakon hare-haren ta’addanci cikin shekaru ukun da suka gabata.
Burkina Faso ce kan gaba da yawan mace-mace saboda ta'addanci, inda ta samu karuwar kashi 68 na adadin wadanda aka kashe, wanda hakan Majalisar ta ce baya rasa nasaba da karancin taimako da kasar ke fuskanta a halin yanzu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI