Masu sanya ido na ƙasa da ƙasa a zaɓen Ghana sun yaba da yadda zaɓen ya gudana

Masu sanya ido na ƙasa da ƙasa a zaɓen Ghana sun yaba da yadda zaɓen ya gudana

Masu sanya idon dai sun bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da suka gudanar a Accra babban birnin ƙasar ta Ghana.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Muhammad Namadi Sambo da ya jagoranci tawagar ECOWAS wajen sanya ido a zaɓen, ya ce an baiwa al’ummar ƙasar dama wajen zaɓen wanda suke so ya jagorance su.

Sama da al’ummar Ghana miliyan 18 ne suka kaɗa ƙuri’a a zaɓen shugaban ƙasa da kuma na ƴan majalisu 276 da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata.

Ku latsa alamar sauti don sauraron rahoton wakilinmu Sham-un Bako........

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Hulda da mu

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI


News Source:   RFI (rfi.fr)