Mai gabatar da ƙara na kotun ICC ya isa Jamhuriyar Congo mai fama da rikici

Mai gabatar da ƙara na kotun ICC ya isa Jamhuriyar Congo mai fama da rikici

Kahn na shirin ganawa da hukumomin Congo, inda ya fara da shugaban ƙasar, Félix Tshisekedi, da sauran manyan mukarraban gwamnati.

Wannan na zuwa ne, yayin da ƙasar ke fama da munana hare-haren /yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan dakarun Rwanda, musamman a gabashin ƙasar.

Kareem Khan daga hagu tare da shugaban Congo, Félix Tshisekedi. Kareem Khan daga hagu tare da shugaban Congo, Félix Tshisekedi. © AFP

A cewar ƙwararu na Majalisar Ɗinkin Duniya, M23 na samun goyon bayan sojojin Rwanda kusan 4,000.

A cikin 'yan makonnin da suka gabata, ƙungiyar ta ƙwace ikon wasu manyan garuruwa biyu a Gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.

Rwanda dai na ci gaba da musanta zzarge-zargen da ake mata na taimakawa 'yan tawayen M23.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Hulda da mu

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI


News Source:   RFI (rfi.fr)