Kungiyar ta ce al’amarin ya rutsa da su lokacin da suke tsaka da aikin bayar da agaji a Rutshutu, mai tazarar kilomita hamsin tsakanin sa da arewacin birnin Goma da ya fada karkashin ikon ‘yan tawayen a makon jiya.
Sai dai kungiyar bata bayyana wadanda ke da alhakin mutuwar jami’an nata ba, amma dai ta ce tana gudanar da bincike a kai.
Ƙungiyar agajin da aka fi sani da HEKS/EPER, na dauke da kaso mai yawa na aikin agajin da ake gudanarwa a gabashin Congo da ma yankunan da ke fama da rikicin masu dauke da makamai.
A halin yanzu dai, ƙungiyar ta ce ta dakatar da ayyukanta a wannan yanki, har sai baba ta gani.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI