Guinea bissau za ta gudanar da babban zaɓe ranar 30 ga watan Nuwamban 2025

Guinea bissau za ta gudanar da babban zaɓe ranar 30 ga watan Nuwamban 2025

Ga dukkanin alamu dai shugaba Emabalo bai damu da caccakar da ake yi masa ba, la’akari da aniyarsa da ya bayyana ta ci gaba da zama kan mulkin Guinea-Bissau har zuwa lokacin da za a zaɓi magajinsa, lamarin da ya ƙara fusata ɓangaren ‘yan adawar da tsohon Fira Minista Domingos Simoes Pereira ke jagoranta.

A cewar ‘yan adawar, ya zama dole shugaba Umaro Sissoco Embalo ya sauka daga mulki a ranar alhamis mai zuwa wato 27 ga watan nan na Fabarairu, domin a lokacin wa’adinsa zai ƙare, duk da cewa a bayan kotun ƙolin ƙasar ta yanke hukuncin cewa sai a ranar 4 ga watan Satumban shekarar nan wa’adin shugaban zai ƙare.

A watan Disambar shekarar bara ta 2024 yakamata a ce zaɓen shugabancin ƙasar ya gudana, amma shugaba Umaro Sissicko ya sanar da ɗage zaɓen a ranar 4 ga watan Nuwamba, ‘yan kwanaki bayan yunƙurin juyin mulkin da gwamnatinsa ta ce an yi.

Sau huɗu aka taɓa yin juyin mulki a Guninea-Bissau yayin da aka yi yunƙurin yin juyin mulkin fiye da sau 10, daga lokacin da ƙasar ta samu ‘yan ci kai daga Portugal a shekarar 1973 zuwa yanzu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Hulda da mu

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI


News Source:   RFI (rfi.fr)