
Wasu majiyoyi na kusa da gwamnatin Faransa ne suka tabbatar da cewa ƙasar ta samu wasiƙar Chadi kan batun janye ɗaukacin sojojinta kafin cikar wa’adin na ƙarshen watan Janairu, sai dai Faransa ta ce tana tattaunawa don ganin ta tsawaita wa’adin.
Bayanai na cewa, wasu manyan jami’an sojojin Faransa, sun ce kwashe sama da dakaru dubu guda da kayan aiki masu tarin yawa daga ƙasar ta tsakiyar Afirka cikin makonni biyu kachal abu ne mai matukar wuya.
Ana kallon matakin gwamnatin Chadi na yanke alakar tsaro da Faransa, a matsayin wata hanyar gayyatar Rasha, to sai dai Shugaban ƙasar Mahamat Deby ya sanar da cewa ƙasar ba ta da niyyar karkata ƙawancenta na tsaro ga wata ƙasa bayan matakinta na katse alaƙar hadin gwiwar sojin da Faransa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI