Al'umma Gabon sun fara fita kada kuri'a a zaban raba gardama

Al'umma Gabon sun fara fita kada kuri'a a zaban raba gardama

An bude runfunan zabe da misalin  karfe 7 na safe agogon kasar inda za’a shafe sa’oi 10 ana kada kuri’a.

Sauyin da ake so a aiwatar ya shafi samar da shugaba mai cikakken iko da zai shafe wa’adin shekaru 7 akan kujera wanda za’a sabuntawa sau guda, sabanin wanda aka  amfani da shi a kasar tsawan shekaru.

A saban kundin tsarin mulki dole ne duk wani dan kasar dake son tsayawa takara shugabancin kasar ya cika tsakanin shekaru 35 zuwa 70 a duniya.

Idan kundin ya samu amincewa zai ba shugaban kasa cikakken ikon tafiyar da majalisar zartaswasa yayin da zai nada mataimaka  biyu da zasu rika dafa masa a ayyukan sa na yau da kullum.  

Wasu daga cikin sauye-sauyen da kundin ya tanada sun hada da soke mukamin Firaminista abunda ke ba shugaban kasar dama sanya ido akan ayukkan ministocin gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Hulda da mu

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI


News Source:   RFI (rfi.fr)